Skip to content
Luka 24:36-49

Luka 24:36-49

36
Suna cikin wannan zance, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu. Sai ya ce musu, “Salama a gare ku!”
37
Suka firgita, suka tsorota, suna tsammani fatalwa ce suka gani.
38
Sai ya ce musu, “Don me kuke damuwa, kuke kuma shakka a zuciyarku?
39
Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
40
Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
41
Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”
42
Suka ba shi ɗan gasasshen kifi,
43
ya karɓa ya ci a gabansu.
44
Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da na gaya muku tun ina tare da ku cewa, dole a cika kome da aka rubuta game da ni, a cikin Dokar Musa, da Annabawa, da kuma Zabura.”
45
Sai ya wayar da tunaninsu don su fahimci Nassi.
46
Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da aka rubuta, cewa dole Kiristi yă sha wahala, a rana ta uku kuma yă tashi daga matattu.
47
Kuma a cikin sunansa za a yi wa’azin tuba da gafarar zunubai, ga dukan ƙasashe. Za a kuwa fara daga Urushalima.
48
Ku ne shaidun waɗannan abubuwa.
49
Zan aika muku da abin da Ubana ya yi alkawari. Amma ku dakata a birnin tukuna, sai an rufe ku da iko daga sama.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options