50
Bayan ya kai su waje kusa da Betani, sai ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.
51
Yana cikin sa musu albarka, sai ya rabu da su. Aka ɗauke shi zuwa cikin sama.
52
Sai suka yi masa sujada, suka koma Urushalima cike da murna sosai.
53
Sai suka ci gaba da zama a cikin haikalin, suna yabon Allah.