Luka 24:36-41
36
Suna cikin wannan zance, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu. Sai ya ce musu, “Salama a gare ku!”
37
Suka firgita, suka tsorota, suna tsammani fatalwa ce suka gani.
38
Sai ya ce musu, “Don me kuke damuwa, kuke kuma shakka a zuciyarku?
39
Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
40
Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
41
Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”
Settings