Skip to content
Luka 23:18-23

Luka 23:18-23

18
Suka yi ihu gaba ɗaya suka ce, “A yi gaba da wannan mutum! A sake mana Barabbas!”
19
(Barabbas yana kurkuku saboda laifin tā da hankali a birnin, da kuma don kisankai.)
20
Sai Bilatus ya sāke yin musu magana don yana so ya saki Yesu.
21
Amma sai suka ci gaba da ihu, suna cewa, “A gicciye shi! A gicciye shi!”
22
Ya sāke ce musu, sau na uku, “Don me? Wane laifi wannan mutum ya yi? Ni dai ban same shi da wani dalilin da ya isa a kashe shi ba. Saboda haka, zan sa a hore shi, sa’an nan in sāke shi.”
23
Amma suna ihu, suna nacewa, suna cewa, dole a gicciye shi, har ihunsu ya rinjaye shi.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options