Tsallake zuwa abun ciki
Luka 20:1-8

An Ƙalubalanci Ikon Yesu

Luka 20:1-8
1
Wata rana da Yesu yana koyar da mutane, yana musu wa’azin bishara a filin haikalin, sai manyan firistoci da malaman dokoki, tare da dattawan suka zo wurinsa.
2
Suka ce masa, “Gaya mana, da wane iko kake yin waɗannan abubuwa. Wa ya ba ka wannan ikon?”
3
Ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku faɗa mini,
4
baftismar Yohanna, daga sama ne ta fito, ko kuwa daga wurin mutane ne?”
5
Sai suka yi shawara da junansu, suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama ne,’ zai tambaya, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’
6
Amma in kuma muka ce, ‘Daga mutane ne,’ dukan mutanen za su jajjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata cewa, Yohanna annabi ne.”
7
Don haka, sai suka amsa cewa, “Ba mu san inda ta fito ba.”
8
Yesu ya ce, “To, ni ma ba zan gaya muku, ko da wane iko ne, nake yin waɗannan abubuwa ba.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options