Skip to content
Luka 15:3

Luka 15:3

Ana nuna aya 3 tare da mahallin da ke kewaye.
1
Yanzu fa, masu karɓar haraji da “masu zunubi” duka suna taruwa don jin koyarwar Yesu.
2
Amma Farisiyawa da malaman dokoki suka yi gunaguni, suna cewa, “Wannan mutum yana karɓan ‘masu zunubi,’ kuma yana ci tare da su.”
3
Sai Yesu ya faɗa musu wannan misali ya ce,
4
“In ɗayanku yana da tumaki ɗari, sa’an nan ɗayansu ta ɓace. Ashe, ba zai bar tasa’in da tara a fili ya je neman wadda ta ɓace, har sai ya same ta ba?
5
In ya same ta, zai sa ta a kafaɗa da murna,
6
ya dawo gida. Sa’an nan zai kira abokansa da maƙwabtansa wuri ɗaya ya ce, ‘Ku taya ni murna, na sami tunkiyana da ta ɓata.’
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 90 chars

Options