Skip to content
Luka 15:1

Luka 15:1

Ana nuna aya 1 tare da mahallin da ke kewaye.
1
Yanzu fa, masu karɓar haraji da “masu zunubi” duka suna taruwa don jin koyarwar Yesu.
2
Amma Farisiyawa da malaman dokoki suka yi gunaguni, suna cewa, “Wannan mutum yana karɓan ‘masu zunubi,’ kuma yana ci tare da su.”
3
Sai Yesu ya faɗa musu wannan misali ya ce,
4
“In ɗayanku yana da tumaki ɗari, sa’an nan ɗayansu ta ɓace. Ashe, ba zai bar tasa’in da tara a fili ya je neman wadda ta ɓace, har sai ya same ta ba?
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 90 chars

Options