Tsallake zuwa abun ciki
Luka 13:18-22

Misalan Girman Mulkin Allah

Luka 13:18-22
18
Sai Yesu ya yi tambaya ya ce, “Yaya mulkin Allah yake? Da me zan kwatanta shi?
19
Yana kama da ƙwayar mustad, wadda wani mutum ya ɗauka, kuma ya shuka a gonarsa. Ta yi girma, ta zama itace, kuma tsuntsayen sararin sama suka huta a rassansa.”
20
Ya sāke tambaya, “Da me zan kwatanta mulkin Allah?
21
Yana kama da yisti wadda mace ta ɗauka, ta kwaɓa garin alkama mai yawa da shi, har sai da yistin ya gauraye kullun duka.”
22
Sa’ad da Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima, sai ya bi ta cikin garuruwan da ƙauyukan, yana koyarwa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options