Skip to content
Luka 12:49-53

Luka 12:49-53

49
“Na zo ne domin in kawo wuta a duniya. Ina so da ta riga ta ƙunu!
50
Amma ina da baftismar da za a yi mini, na kuwa damu sosai, sai na kammala ta!
51
Kuna tsammani na zo domin in kawo salama a duniya ne? A’a! Ina gaya muku, rabuwa ne.
52
Daga yanzu, za a iske mutum biyar a gida ɗaya sun rabu, suna gāba da juna, uku suna gāba da biyu, biyun suna gāba da ukun.
53
Za su rarrabu. Mahaifi yana gāba da ɗan, ɗan kuma yana gāba da mahaifin. Mahaifiya tana gāba da diyar, diyar kuma tana gāba da mahaifiyar. Suruka tana gāba da matar ɗa, matar ɗa kuma tana gāba da suruka.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options