Luka 12:49-52
49
“Na zo ne domin in kawo wuta a duniya. Ina so da ta riga ta ƙunu!
50
Amma ina da baftismar da za a yi mini, na kuwa damu sosai, sai na kammala ta!
51
Kuna tsammani na zo domin in kawo salama a duniya ne? A’a! Ina gaya muku, rabuwa ne.
52
Daga yanzu, za a iske mutum biyar a gida ɗaya sun rabu, suna gāba da juna, uku suna gāba da biyu, biyun suna gāba da ukun.
Settings