Skip to content
Luka 1:59-66

Luka 1:59-66

59
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options