Mahukunta 1:22-26
22
To, gidan Yusuf suka auka wa Betel, Ubangiji kuwa yana tare da su.
23
Sa’ad da suka aike mutane don su leƙi asirin Betel (da dā ake kira Luz),
24
’yan leƙen asirin suka ga wani ya fito daga birnin sai suka ce masa, “Ka nuna mana yadda za mu shiga birnin, mu kuwa za mu yi maka alheri.”
25
Saboda haka ya nuna musu, suka kuwa hallaka birnin, suka bar mutumin da dukan iyalinsa da rai.
26
Sa’an nan ya tafi ƙasar Hittiyawa, inda ya gina birni ya kuma kira shi Luz, haka ake kira birnin har wa yau.
Settings