Yunana 3:1-4
1
Sa’an nan sai maganar Ubangiji ta zo wa Yunana sau na biyu.
2
“Tafi babban birnin nan Ninebe, ka yi masa shelar saƙon da na ba ka.”
3
Sai Yunana ya yi biyayya da maganar Ubangiji, ya tafi Ninebe. Ninebe birni ne da yake da muhimmanci, wanda sai an ɗauki kwana uku kafin a iya zaga shi.
4
A rana ta fari, Yunana ya kama tafiya yana ratsa birnin. Sai ya yi shela cewa, “Nan da kwana arba’in za a hallaka Ninebe?”
Settings