Yohanna 9:10-12
10
Sai suka ce, “To, yaya aka yi idanunka suka buɗe?”
11
Ya amsa ya ce, “Mutumin da ake kira Yesu ne ya kwaɓa laka ya shafa mini a idanu. Ya ce mini in je Silowam in wanke. Na kuwa tafi, na wanke, sai na sami ganin gari.”
12
Suka tambaye shi suka ce, “Ina mutumin yake?” Ya ce, “Ban sani ba.”