Yohanna 9:1-5
1
Da Yesu yana tafiya, sai ya ga wani mutum wanda aka haifa makaho.
2
Sai almajiransa suka tambaye shi suka ce, “Rabbi, wane ne ya yi zunubi, mutumin ne, ko iyayensa, da ya sa aka haife shi makaho?”
3
Sai Yesu ya ce, “Ba don mutumin ko iyayensa sun yi zunubi ne ba, sai dai don a bayyana aikin Allah ne a rayuwarsa.
4
Muddin da sauran rana, dole mu yi aikin wanda ya aiko ni. Dare yana zuwa, sa’ad da ba wanda zai iya yin aiki.
5
Yayinda ina a cikin duniya, ni ne hasken duniya.”
Settings