Yohanna 14:12-15
12
Gaskiya nake gaya muku, duk wanda yake da bangaskiya gare ni, zai yi abubuwan da ni nake yi. Zai ma yi abubuwa masu girma fiye da waɗannan, don zan tafi wurin Uba.
13
Kuma zan yi duk abin da kuka roƙa cikin sunana, don Ɗan ya kawo ɗaukaka ga Uban.
14
Za ku iya roƙe ni kome a cikin sunana, zan kuwa yi.
15
“In kuna ƙaunata za ku yi biyayya da umarnina.
Settings