Skip to content
Yohanna 1:6-13

Yohanna 1:6-13

6
Akwai wani mutumin da aka aiko daga Allah; mai suna Yohanna.
7
Ya zo a matsayin mai shaida domin yă ba da shaida game da wannan haske, don ta wurinsa dukan mutane su ba da gaskiya.
8
Shi kansa ba shi ne hasken ba; sai dai ya zo a matsayin shaida ne kaɗai ga hasken.
9
Haske na gaskiya da yake ba da haske ga kowane mutum mai shigowa duniya.
10
Yana a duniya, kuma ko da yake an yi duniya ta wurinsa ne, duniya ba tă gane shi ba.
11
Ya zo wurin abin da yake nasa, amma nasa ɗin ba su karɓe shi ba.
12
Duk da haka dukan waɗanda suka karɓe shi, ga waɗanda suka gaskata a sunansa, ya ba su iko su zama ’ya’yan Allah
13
’ya’yan da aka haifa ba bisa hanyar ’yan adam, ko shawarar mutum ko nufin namiji ba, sai dai haifaffu bisa ga nufin Allah.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options