Tsallake zuwa abun ciki
Ayuba 7:6-10

Ayuba 7:6-10

6
“Kwanakina suna wucewa da sauri, fiye da yadda ƙoshiyar masaƙa take wucewa da sauri, za su kawo ga ƙarshe ba bege.
7
Ka tuna, ya Allah, raina numfashi ne kawai; idanuna ba za su taɓa sāke ganin farin ciki ba.
8
Idanun da suke ganina yanzu ba za su sāke ganina ba; za ku neme ni amma ba za ku same ni ba.
9
Kamar yadda girgije yakan ɓace yă tafi, haka mutum yake shige zuwa kabari ba kuwa zai dawo ba.
10
Ba zai taɓa zuwa gidansa ba; ba za a sāke san da shi ba.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options