Ayuba 6:1-4
1
Sa’an nan Ayuba ya amsa,
2
“Da kawai za a iya auna wahalata a kuma sa ɓacin raina a ma’auni!
3
Ba shakka da sun fi yashin teku nauyi, shi ya sa nake magana haka.
4
Kibiyoyin Maɗaukaki suna a kaina, ruhuna yana shan dafinsa; fushin Allah ya sauka a kaina.