Ayuba 6:8-13
8
“Kash, da ma Allah zai ba ni abin da nake fatar samu, da ma Allah zai biya mini bukatata,
9
wato, Allah yă kashe ni, yă miƙa hannunsa yă yanke raina!
10
Da sai in ji daɗi duk zafin da nake sha ban hana maganar Mai Tsarkin nan cika ba.
11
“Wane ƙarfi nake da shi, har da zan ci gaba da sa zuciya? Wane sa zuciya ne zai sa in yi haƙuri?
12
Da ƙarfin dutse aka yi ni ne? Ko jikina tagulla ne?
13
Ina da wani ikon da zan iya taimakon kai na ne, yanzu da aka kore nasara daga gare ni?
Settings