Ayuba 41:22-34
22
Akwai ƙarfi a cikin wuyanta; razana tana wucewa a gabanta.
23
Namanta yana da kauri a manne da juna; naman yana da tauri ba ya matsawa.
24
Ƙirjinta yana da ƙarfi kamar dutse, da ƙarfi kamar dutsen niƙa.
25
Sa’ad da ta tashi, manya suna tsorata; suna ja da baya.
26
Takobi ba ta iya yankanta, kibiya ko māshi ba sa iya huda ta.
27
Ƙarfe kamar kara ne a wurinta tagulla kuma kamar ruɓaɓɓen katako ne a wurinta.
28
Māsu ba su sa ta tă gudu; jifar majajjawa kamar na ciyawa ne gare ta.
29
Kulki a gare ta kamar ciyawa ne, tana dariyar wucewar māshi.
30
Cikinta yana rufe a ɓawo masu ƙarfi, tana kabtar ƙasa in tana tafiya.
31
Tana sa zurfin kogi yă tafasa kamar tukunya, ta kuma sa teku yă zama kamar tukunyar man shafawa.
32
A bayanta ya bar haske kamar zurfin ruwan da yana kumfa.
33
Ba wani abu kamar ta a duniya, halitta marar tsoro.
34
Tana rena duk masu girman kai. Ita take mulki kan duk masu girman kai.”
Settings