Ayuba 40:6-13
6
Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
7
“Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
8
“Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
9
Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
10
Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
11
Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
12
Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
13
Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
Settings