Ayuba 4:12-17
12
“Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
13
Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
14
Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
15
Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
16
Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
17
‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
Settings