Skip to content
Ayuba 39:1-8

Ayuba 39:1-8

1
“Ka san lokacin da awakin kan dutse suke haihuwa? Ko ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa?
2
Kana ƙirga watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin da suke haihuwa?
3
Suna kwanciya su haifi ’ya’yansu; naƙudarsu ta ƙare bayan sun haihu.
4
’Ya’yansu suna girma kuma suna girma cikin ƙarfi a jeji; sukan tafi ba su dawowa.
5
“Wane ne yake sakin jakin dawa yă bar shi? Wane ne yake kunce igiyoyinsu?
6
Na sa jeji yă zama gidansa ƙasar gishiri kuma ta zama wurin zamansa.
7
Yana dariyar hargitsin da yake faruwa a cikin gari; ba ya jin tsawar mai tuƙa shi.
8
Yana kiwo a kan tuddai don abincinsa yana neman kowane ɗanyen abu mai ruwan ciyawa.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options