Skip to content
Ayuba 38:39

Ayuba 38:39

Ana nuna aya 39 tare da mahallin da ke kewaye.
36
Wane ne yake cika zuciya da hikima ko kuma yake ba zuciya ganewa?
37
Wane ne yake da hikimar iya ƙirga gizagizai? Wane ne zai iya karkato bakunan tulunan sammai
38
sa’ad da ƙura ta yi yawa ta daskare a wuri ɗaya?
39
“Za ka iya farauto wa zakanya nama, ka kuma kawar wa zakoki yunwarsu.
40
Lokacin da suka kwanta cikin kogunansu, ko kuma lokacin da suke a wurin ɓuyansu?
41
Wane ne yake ba hankaka abinci lokacin da ’ya’yansa suke kuka ga Allah, kuma suna yawo don rashin abinci?
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options