Ayuba 36:27-30
27
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa ’yan adam a wadace.
29
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.