Skip to content
Ayuba 36:26-32

Ayuba 36:26-32

26
Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa ’yan adam a wadace.
29
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
31
Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
32
Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options