Skip to content
Ayuba 36:16-21

Ayuba 36:16-21

16
“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
17
Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
18
Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
19
Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
20
Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
21
Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options