Skip to content
Ayuba 20:4-9

Ayuba 20:4-9

4
“Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
5
mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
6
Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
7
Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
8
Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
9
Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options