Skip to content
Ayuba 20:12-21

Ayuba 20:12-21

12
“Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
13
ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
14
duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
15
Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
16
Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
17
Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
18
Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
19
Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
20
“Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
21
Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options