Ayuba 19:13-16
13
“Ya raba ni da ’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.