Ayuba 19:1-9
1
Sai Ayuba ya amsa,
2
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
3
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
4
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
5
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
6
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
7
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
8
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
9
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
Settings