Skip to content
Ayuba 18:15-21

Ayuba 18:15-21

15
Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
16
Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
17
An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
18
An tura shi daga cikin haske zuwa cikin duhu, an kore shi daga duniya.
19
Ba shi da ’ya’ya ko zuriya cikin mutanensa, ba sauran wanda yake a raye a wurin da ya taɓa zama.
20
Mutanen Yamma suna mamakin abin da ya faru da shi; tsoro ya kama mutanen gabas.
21
Ba shakka haka wurin zaman mugun mutum yake, haka wurin zaman wanda bai san Allah ba yake.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options