Ayuba 18:5-17
5
“An kashe fitilar mugu; harshen wutarsa ya daina ci.
6
Wutar cikin tentinsa ta zama duhu; fitilar da take kusa da shi ta mutu.
7
Ƙarfin takawarsa ya ragu; dabararsa ta ja fāɗuwarsa.
8
Ƙafafunsa sun kai shi cikin raga, yana ta yawo a cikin ragar.
9
Tarko ya kama ɗiɗɗigensa; tarko ya riƙe shi kam.
10
An ɓoye masa igiya da za tă zarge shi a ƙasa; an sa masa tarko a kan hanyar da zai bi.
11
Tsoro duk ya kewaye shi ta kowane gefe yana bin shi duk inda ya je.
12
Masifa tana jiransa; bala’i yana shirye yă fāɗa masa a lokacin da zai fāɗi.
13
Ya cinye wani sashe na gaɓar jikinsa; ɗan fari na mutuwa ya cinye ƙafafunsa.
14
An yage shi daga zaman lafiyar da yake yi a cikin tentinsa aka sa shi tsoro sosai.
15
Wuta ta cinye tentinsa; farar wuta ta rufe wurin da yake zama.
16
Jijiyoyinsa sun bushe a ƙasa rassansa sun mutu a sama.
17
An manta da shi a duniya; ba wanda yake ƙara tunawa da shi.
Settings