Ayuba 18:1-4
1
Sai Bildad mutumin Shuwa ya amsa,
2
“Yaushe za ka gama maganganun nan? Ka dawo da hankalinka sa’an nan za mu iya yin magana.
3
Don me muke kamar shanu a wurinka, ka ɗauke mu mutanen wofi?
4
Kai da ka yayyage kanka don haushi, za a yashe duniya saboda kai ne? Ko kuma duwatsu za su matsa daga wurinsu?
Settings