Skip to content
Ayuba 17:11-16

Ayuba 17:11-16

11
Kwanakina sun wuce, shirye-shiryena sun ɓaci haka kuma abubuwan da zuciyata take so.
12
Mutanen nan sun juya rana ta zama dare. A tsakiyar duhu suka ce, ‘Haske yana kusa.’
13
In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu,
14
In na ce wa kabari, ‘Kai ne mahaifina,’ tsutsa kuma ke ce, ‘Mahaifiyata’ ko ‘’yar’uwata,’
15
To, ina begena yake? Wane ne zai iya ganin wani bege domina?
16
Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options