Tsallake zuwa abun ciki
Irmiya 13:22-27

Halin zunubi marar magani

Irmiya 13:22-27
22
In kuma kuka tambaye kanku “Me ya sa wannan ya faru da mu?” Wannan kuwa saboda yawan zunubanku ne ya sa fatarinku ya yage aka kuma wahalshe jikinku.
23
Mutumin Habasha zai iya canja launin fatar jikinsa ko damisa ta canja dabbare dabbarenta? Ba za ku iya yin alheri ku da kuka saba da yin mugunta ba.
24
“Zan watsar da ku kamar yayin da iskar hamada take hurawa.
25
Rabonku ne wannan, sashen da na auka muku,” in ji Ubangiji “domin kun manta da ni kuka kuma dogara ga allolin ƙarya.
26
Zan kware fatarinku sama ya rufe fuskarku don a iya ga tsiraicinku
27
zinace zinacenku da haniniya kamar dawakai, karuwancinku na bankunya! Na ga ayyukanku na banƙyama a kan tuddai da kuma a filaye. Kaitonki, ya Urushalima! Har yaushe za ki ci gaba da rashin tsarki?”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options