Skip to content
Ishaya 10:28-32

Ishaya 10:28-32

28
Sun shiga Ayiyat; sun bi ta Migron; sun adana tanade-tanade a Mikmash.
29
Suka ƙetare ta hanya, suka kuma ce, “Za mu kwana a Geba.” Rama ta firgita; Gibeya ta Shawulu ta gudu.
30
Ki yi ihu, ya Diyar Gallim! Ki saurara, ya Layisha! Kayya, Anatot abin tausayi!
31
Madmena tana gudu; mutanen Gebim sun ɓuya.
32
A wannan rana za su dakata a Nob; za su jijjiga ƙarfinsu a dutsen Diyar Sihiyona, a tudun Urushalima.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options