Tsallake zuwa abun ciki
Hosiya 4:15-19

Gargaɗi ga Yahuza

Hosiya 4:15-19
15
“Ko da yake kun yi zina, ya Isra’ila, kada Yahuda ya yi laifi. “Kada ku tafi Gilgal; kada ku haura zuwa Bet-Awen. Kuma kada ku rantse cewa, ‘Muddin Ubangiji yana a raye!’
16
Isra’ilawa masu taurinkai ne, kamar karsana mai taurinkai. Yaya Ubangiji zai iya kiwonsu kamar tumaki a makiyaya mai ɗanyar ciyawa?
17
Efraim ya haɗa kai da gumaka; ku ƙyale shi kurum!
18
Ko ma sa’ad da abin shansu ya ƙare, sai suka ci gaba da karuwancinsu; masu mulkinsu suna ƙaunar abin kunya.
19
Guguwa za tă share su, hadayunsu kuma za su jawo musu abin kunya.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options