Hosiya 13:4-8
4
“Amma ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar. Ba za ku yarda da wani Allah ba sai ni, ba wani Mai Ceto in ban da ni.
5
Na lura da ku a hamada, cikin ƙasar mai ƙunar zafi.
6
Sa’ad da na ciyar da su sun ƙoshi; sa’ad da suka ƙoshi, sai suka fara taƙama; sai suka manta da ni.
7
Saboda haka zan hau kansu kamar zaki, zan ɓuya a bakin hanya kamar damisa.
8
Kamar beyar da aka ƙwace mata ’ya’yanta, zan fāɗa musu in ɓarke su. Kamar zaki zan cinye su; kamar naman jeji zan yayyage su.
Settings