Skip to content
Hosiya 12:3-6

Misalin Yakubu, Kakan Isra’ila

Hosiya 12:3-6
3
A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
4
Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
5
Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
6
Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
Settings

Reading style

Typeface

Font size 19px

Reading width 90 chars

Options