Skip to content
Farawa 33:12-16

Farawa 33:12-16

12
Sa’an nan Isuwa ya ce, “Bari mu tafi, zan yi maka rakiya.”
13
Amma Yaƙub ya ce masa, “Ranka yă daɗe, ka san cewa ’ya’yan ƙanana ne, dole in lura da tumaki da shanun da suke shayar da jariransu. In aka kore su da gaggawa a rana guda kaɗai, dukan dabbobin za su mutu.
14
Saboda haka bari ranka yă daɗe yă sha gaban bawansa, ni kuma in tafi a hankali bisa ga saurin abin da ake kora a gabana da kuma saurin ’ya’yan, sai na iso wurinka ranka yă daɗe, a Seyir.”
15
Sai Isuwa ya ce, “To, bari in bar waɗansu mutanena tare da kai.” Yaƙub ya ce, “Amma me ya sa za ka yi haka? Bari dai in sami tagomashi a idanunka ranka yă daɗe.”
16
Saboda haka a wannan rana Isuwa ya kama hanyar komawa zuwa Seyir.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options