Skip to content
Farawa 21:1-6

Farawa 21:1-6

1
Ana nan sai Ubangiji ya nuna wa Saratu alheri kamar yadda ya ce, Ubangiji kuma ya yi wa Saratu abin da ya yi alkawari.
2
Saratu ta yi ciki, ta kuma haifa wa Ibrahim ɗa a tsufansa; a daidai lokacin da Allah ya yi masa alkawari.
3
Ibrahim ya sa wa ɗan da Saratu ta haifa masa suna Ishaku.
4
Sa’ad da ɗansa Ishaku ya kai kwana takwas da haihuwa, sai Ibrahim ya yi masa kaciya, kamar yadda Allah ya umarce shi.
5
Ibrahim yana da shekara ɗari, sa’ad da aka haifa masa ɗansa Ishaku.
6
Saratu ta ce, “Allah ya sa na yi dariya, kuma duk wanda ya ji game da wannan, zai yi dariya tare da ni.”
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options