Tsallake zuwa abun ciki
Afisawa 4:17-24

Cire tsohon mutum

Afisawa 4:17-24
17
To, ina dai faɗa muku, ina kuma nace faɗa muku a cikin Ubangiji, cewa kada ku ci gaba da yin rayuwa kamar yadda Al’ummai suke yi, masu banzan tunani.
18
Suna a cikin duhu a fahimtarsu, kuma a rabe suke daga ran Allah saboda jahilcin da yake cikinsu ta dalilin taurarewar zukatansu.
19
Ba sa damu da wani abu ko mai kyau ko marar kyau. Rayukansu sun cika da kowace irin ƙazanta da haɗama.
20
Amma ba abin da aka koya muku ke nan ba sa’ad da kuka zo ga sanin Kiristi.
21
Da yake kun ji duka game da shi, kuka kuma koyi gaskiyar da take cikin Yesu,
22
sai ku tuɓe tsohon mutumin nan naku da kuma rayuwarku ta dā, wadda take lalacewa saboda sha’awace-sha’awacen da suke ruɗe ku.
23
A maimakon haka, bari Ruhu yă sabunta tunaninku da kuma halayenku.
24
Ku sanya sabon halin nan da aka halitta bisa ga kamannin Allah, halin nan kuwa, yă bayyana cikin adalci, da zaman tsarki.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options