Tsallake zuwa abun ciki
Maimaitawar Shari’a 5:29-33

Allah ya yaba da niyyar Isra’ila

Maimaitawar Shari’a 5:29-33
29
Kash, da a ce zukatansu za su zama masu tsorona, su kuma kiyaye dukan dokokina kullum mana, saboda kome yă zama da lafiya gare su, da kuma ’ya’yansu har abada!
30
“Je, ka faɗa musu su koma tentunansu.
31
Kai kuwa ka tsaya a nan tare da ni saboda in ba ka umarnai, ƙa’idodi da kuma dokoki duka, da za ka koya musu don su bi a ƙasar da nake ba su, su mallaka.”
32
Sai ku yi hankali don ku yi abin da Ubangiji Allahnku ya umarce ku; kada ku juya dama ko hagu.
33
Ku yi tafiya cikin dukan hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, saboda ku zauna, ku yi nasara, ku kuma yi tsawon rai a ƙasar da za ku mallaka.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options