Tsallake zuwa abun ciki
Maimaitawar Shari’a 30:11-14

Sauƙin Samun Umarnin Allah

Maimaitawar Shari’a 30:11-14
11
To, abin da nake umartanku a yau, ba mai wuya ba ne gare ku, ba kuma abin da ya fi ƙarfinku ba ne.
12
Ba ya can sama, balle ku ce, “Wa zai hau sama yă kawo mana, yă kuma furta mana, don mu yi biyayya?”
13
Ba kuwa yana gaba da teku ba, da za ku ce, “Wa zai haye tekun don yă kawo mana, yă kuma furta mana, don mu yi biyayya?”
14
A’a, kalmar tana nan dab da ku, tana cikin bakinku da cikin zuciyarku, don ku yi biyayya.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options