Tsallake zuwa abun ciki
Maimaitawar Shari’a 16:18-20

Kafa Adalci da Iko

Maimaitawar Shari’a 16:18-20
18
Ku naɗa alƙalai da shugabanni don kowace kabila, a kowane birnin da Ubangiji Allahnku yake ba ku, za su kuma shari’anta mutane ba nuna bambanci.
19
Kada ku ɓata shari’a, ko ku nuna bambanci. Kada ku karɓi cin hanci, gama cin hanci yakan makanta idanu mai hikima, yă murɗe maganar mai gaskiya.
20
Gaskiya ce kaɗai za ku bi don ku rayu, ku kuma mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Reading Width 45 chars

Options