18
Mata, ku yi biyayya ga mazanku, yadda ya dace cikin Ubangiji.
19
Maza, ku ƙaunaci matanku kada ku nuna musu hali marar tausayi.
20
’Ya’ya, ku yi biyayya ga iyayenku cikin kome, gama wannan yakan gamshi Ubangiji.
21
Ubanni, kada ku matsa wa yaranku lamba, don kada su fid da zuciya.