Skip to content
1 Timoti 2:9-15

1 Timoti 2:9-15

9
Ina kuma so mata su lura su yi wa kansu adon da ya cancanta, da rigunan da suka dace, ba da adon kitso ko sa kayan zinariya ko lu’ulu’u ko kuma tufafi masu tsada ba,
10
sai dai su yi ayyuka masu kyan da suka dace da matan da suke masu bauta wa Allah.
11
Ya kamata mace ta riƙa koyo cikin natsuwa da cikakkiyar biyayya.
12
Ban ba mace izini ta koyar ko tă yi mulki a kan namiji ba; sai dai ta zauna shiru.
13
Gama Adamu ne aka fara halitta, sa’an nan Hawwa’u.
14
Ba kuma Adamu ne aka yaudara ba; macen ce aka yaudara ta kuma zama mai zunubi.
15
Amma mata Za tă sami ceto za su sami ceto ta wurin haihuwa, in suka ci gaba cikin bangaskiya, ƙauna da kuma tsarki tare da halin sanin ya kamata.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options