Skip to content
1 Timoti 2:1-7

1 Timoti 2:1-7

1
Da farko dai, ina gargaɗe ku cewa a yi roƙe-roƙe, ana addu’o’i, ana yin addu’a a madadin waɗansu da kuma a yi godiya saboda kowane mutum
2
da sarakuna da dukan masu mulki, domin mu zauna lafiya, rai kuma kwance, muna bin Allah sosai a cikin natsuwa.
3
Wannan yana da kyau, yakan kuma gamshi Allah Mai Cetonmu,
4
wanda yake so dukan mutane su sami ceto su kuma zo ga sanin gaskiya.
5
Gama Allah ɗaya ne, matsakanci kuma ɗaya tsakanin Allah da mutane, shi ne kuwa Kiristi Yesu,
6
wanda ya ba da kansa fansa domin dukan mutane, shaidar da aka bayar a daidai lokaci.
7
Don haka ne aka sa ni mai wa’azi, da manzo kuma, gaskiya nake faɗa, ba ƙarya ba, na kuma zama malami mai koya wa al’ummai al’amarin bangaskiya da kuma na gaskiya.
Settings

Reading Style

Typeface

Font Size 19px

Options